26 Afirilu 2026 - 09:47
Source: ABNA24
Mutane Hudu Sun Yi Shahada A Hare-Haren Isra'ila A Kudancin Lebanon

Hare-haren Isra'ila sun kashe akalla mutane hudu a gundumar Nabatieh ta kudancin Lebanon, a cewar kamfanin dillancin labarai na gwamnati, yayin da Isra'ila ke ci gaba da hare-harenta duk da tsawaita tsagaita wuta da Hizbullah na tsawon makonni uku.

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa: Kamfanin dillancin labarai na Lebanon (NNA) ya ruwaito a ranar Asabar cewa hare-haren Isra'ila guda biyu, daya ya afkawa wata babbar mota da kuma wani da ya afkawa babur a garin Yohmor al-Shaqif, sun yi sanadiyar mutuwar mutane hudu.

NNA ta kuma ce sojojin Isra'ila sun kai hare-haren bindigu a yau a yankunan Qantara, Qusayr, Wadi Hassan, Yohmor al-Shaqif, da Houla. Wadannan hare-hare su ne na baya-bayan nan da suka girgiza kudancin Lebanon tun bayan da Donald Trump ya sanar da tsawaita tsagaita wuta a ranar Alhamis.

A halin da ake ciki, a cikin garin Bint Jbeil na kudancin Lebanon, an bayar da rahoton cewa sojojin Isra'ila sun rusa gine-gine da bama-bamai a safiyar yau Asabar.

Manema labarai na Al Jazeera daga fagen daga sun kuma bayar da rahoton fashewar gidaje da gine-gine a cikin garin Khiyam.

Your Comment

You are replying to: .
captcha